![]() |
|
2019-07-05 10:31:28 cri |
Yayin taron mai taken " gina kyakkyawar makoma ta bai daya ga daukacin bil-Adama da gina makoma mai haske ga ilimin sana'o'i na kasashen Sin da Afirka, ana sa ran mahalartansa za su tattauna yadda ilimin sana'o'i zai hanzarta raya nahiyar Afirka.
A wasikar da ya aikewa taron, mataimakin babban darektan cibiyar musaya tsakanin al'ummomin kasa da kasa ta kasar Sin a ma'aikatar Ilimin kasar Yang Xiaochun, ya ce, yana fatan za a tsara matakai tare da bullo da hanyoyi na hadin gwiwar ilimin sana'o'i tsakanin Sin da kasashen dake gabashin Afirka.
Taron na kwanaki biyu, ya samu halartar cibiyoyi 16 daga kasar Sin da kuma 40 daga Afirka.(Ibrahim)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China