Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Sakataren MDD ya yi maraba da sanarwar sake dawo da tattaunawa tsakanin DPRK da Amurka
2019-07-01 10:06:34        cri

Babban sakataren MDD Antonio Guterres ya yi maraba da jin sanarwar cewa, kasar Koriya ta arewa (DPRK) da Amurka za su sake dawo da yin tattaunawa a tsakaninsu.

Mai magana da yawun Guterres, Stephane Dujarric wanda ya bayyana hakan cikin wata sanarwa, ya ce, Antonio Guterres ya yi maraba da yadda shugabannin Amurka da Koriya suka gana a kauyen Panmunjom, musamman sanarwar cewa, Koriya ta arewa da Amurka za su sake dawo da tattaunawa a tsakaninsu.

Ya ce, babban sakataren yana goyon bayan kokarin da sassan biyu ke yi, na kulla sabuwar alakar wanzar da zaman lafiya mai dorewa, da tsaro da ma kawar da makaman nukiliya kwata-kwata daga zirin Koriya.

An ruwaito shugaba Donald Trump na Amurka a jiya Lahadi yana cewa, wasu tawagogi daga kasashen Amurka da Koriya ta rewa, za su fara ganawa " nan da makonni biyu ko uku" inda za su tattauna kan shirin nukiliyar kasar Koriya ta arewa, amma ya ce, ba ya gaggawar cimma yarjejeniya.(Ibrahim)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China