Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Sin za ta fitar da jerin sassan da ke da rauni ta fuskar cinikayya in ji ma'aikatar cinikayya
2019-05-31 19:06:22        cri
Kakakin ma'aikatar cinikayyar kasar Sin Gao Feng, ya ce za a fitar da sassan kamfanoni, da sauran abokan huldar kasar Sin da ke da rauni a fannin hada hadar cinikayya da kasar.

Kamfanonin da abokan huldar da za su shiga wannan jerin sunaye, sun kunshi kamfanonin waje da kungiyoyi da daidaikun mutane da ba sa martaba dokokin kasuwa, ko wadanda suka karya ka'idojin kwangila, ko suka katse samar da hajojin bukata ga kamfanonin Sin bisa dalilan da ba na cinikayya ba. Sauran sun hada da wadanda suka gurgunta moriyar halal ta kamfanonin Sin.

Mr. Gao ya ce nan gaba kadan, za a fitar da cikakkun bayanai, game da matakan da za a dauka kan irin wadannan kamfanoni.(Saminu)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China