2019-05-27 21:06:11 cri |
Jami'in ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, an kashe 'ya'yan kungiyar ta JTF biyar da wasu kauyawa 11, lokacin da mayakan Boko Haram suka farma wasu kauyuka biyu dake wajen Maiduguri, fadar mulkin jihar Borno a jiya Lahadi.
Ya ce, mutane da dama ne suka jikkata sanadiyar harin. Galibin kauyawan dai sun gudu zuwa cikin daji don tsira da rayukansu, yayin da maharan ke harbin kan mai uwa da wabi.(Ibrahim)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China