Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
WHO ta yi Allah wadai da kisan jami'an kiwon lafiya a Tripoli
2019-05-26 21:05:27        cri
Hukumar lafiya ta duniya (WHO) ta yi Allah wadai da kashe wasu jami'an kiwon lafiya biyu a Tripoli babban binin kasar Libya, inda ake cigaba da fuskantar tashin hankali tsakanin dakarun tsaron gwamnati dake samun goyon bayan MDD da dakarun sojojin dake da sansani a gabashin kasar.

"Hukumar WHO a Libya tayi Allah wadai da kashe jami'an lafiyar biyu a ranar Alhamis a Tripoli a lokacin da aka samu barkewar rikicin wanda ya rutsa da motocin daukar marasa lafiya biyu. Kana wasu jami'an dake kula da motoci da dama suka jikkata," in ji WHO a sakonta na twitter.

An lalata motocin daukar marasa lafiyar biyu a kudancin Tripoli a daidai lokacin da suke gaggawar zuwa ceton mutanen da suka jikkata a sakamakon fadan da ya barke, inji WHO.

Dakarun sojojin, wanda Khalifa Haftar ke jagoranta, suna cigaba da daukar matakan soji tun a farkon watan Afrilu a yunkurinsu na neman kwace ikon babban birnin kasar daga hannun gwamnati.

WHO tace kawo yanzu tashin hankalin yayi sanadiyyar mutuwar mutane 510 tare da jikkata wasu mutanen kimanin 2,467.

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China