2019-05-20 09:48:49 cri |
Kwamitin ya fada cikin wata sanarwa cewa, mambobin kwamitin, sun yi Allah wadai da babbar murya kan harin wanda aka kaddamar da shi a ranar Asabar kan motocin jami'an shirin wanzar da zaman lafiyar MDD a Mali (MINUSMA) a yankunan Timbuktu da Tessalit.
An hallaka wani jami'in wanzar da zaman lafiya na Najeriya da kuma jikkata wani yayin da maharan suka kaddamar da harin a Timbuktu, dake arewacin Mali. Haka lamarin ya kasance a yankin Tessalit inda aka raunata wasu jami'an shirin wanzar da zaman lafiyar 3 'yan kasar Chadi.
Sanarwar ta ce, "Mambobin kwamitin sulhun MDD sun bayyana damuwarsu game da yanayin tsaro da ake ciki a Mali da kuma barazanar tsaro na hare haren ta'addanci da ake fuskanta a yankin Sahel. Sun bukaci dukkan bangarorin Mali da su aiwatar da yarjejeniyar zaman lafiyar Mali ba tare da bata lokaci ba." (Ahmad)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China