Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Firaministan Sin ya yi kira da a kara kwazo wajen daga martabar tambarin kasar Sin
2019-05-10 21:14:02        cri
Firaministan kasar Sin Li Keqiang, ya yi kira da a kara kwazo wajen daga martabar tambarin hajojin kasar Sin a dukkanin kasashen duniya, ta hanyar bunkasa kwarewa da sanin makamar aiki. Li Keqiang ya bayyana hakan ne cikin wani sakon umarni da ya aike a Juma'ar nan, ga taron ranar tambarin kasar Sin wanda aka bude a birnin Shanghai.

Ya ce karfafa kimar tambarin Sin, da bunkasa sashen masana'antun sarrafa hajoji, da inganta sashen ba da hidima na da muhimmancin gaske, wajen bunkasa harkokin sayayya a cikin gida, da bunkasa ci gaba mai ma'ana.

Taron ranar tambarin kasar Sin wanda aka bude a birnin Shanghai, zai gudana tsakanin ranekun 10 zuwa 12 ga watan nan na Mayu.

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China