Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
MDD: Tashin hankali a yankin Sahel ya kazanta
2019-05-09 10:18:10        cri
Manyan jami'an MDD sun yi gargadin cewa tabarbarewar tsaro da hare-haren masu dauke da makamai a yankin Sahel ya yi matukar muni, kakakin MDD ne ya bayyana hakan a ranar Laraba.

Jami'an MDD sun bukaci a kara samar da kayayyakin jin kai ga miliyoyin mutanen da tashin hankalin da ya barke ya shafa, in ji Farhan Haq, mataimakin kakakin sakatare-janar na MDD Antonio Guterres.

A cewar Haq, masu gudanar da ayyukan jin kai dake zaune a kasashen Burkina Faso, Mali da Nijer sun yi gargadin cewa bukatar kayayyakin tallafin jin kai da ake da shi ya zarta abin da ake da shi a hannu, a yayin da tashe-tashen hankula ke ci gaba da kara kamari da kuma barazanar dake ci gaba da bazuwa zuwa sassan gabar tekun kasashen yammacin Afrika.

Adadin matsalolin tsaro da suka faru a Burkina Faso, Mali da yammacin jamhuriyar Nijer ya sake karuwa matuka a cikin watannin baya bayan nan, inda aka samu tashe-tashen hankula sama da 150 a cikin watan Afrilu kadai wadanda suka yi sanadiyyar rayukan sama da mutane 300. (Ahmad Fagam)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China