Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
An bude taron kolin fasahar zamani na kasar Sin a lardin Fujian
2019-05-07 06:51:27        cri

A yau ne aka bude taron kolin fasahohin zamani na kasar Sin karo na biyu a Fuzhou, babban birnin lardin Fujian dake gabashin kasar, inda aka baje kolin sabbin na'urorin zamani da suka karade sassa da kamfanonin gwamnatin kasar.

Cikin fasahohin da ake amfani da su a bikin dake gudana a birnin Fuzhou, sun hada da motoci marasa matuka da na'urorin tsaro na tantance fuska zuwa fasahar sadarwa ta 5G. Za kuma a gabatar da rahoton bincike game da nasarar da kasar Sin ta samu a fannin kera fasahohin zamani a shekarar 2018.(Ibrahim)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China