MINUSMA ta bukaci a sako shugaban rikon kwaryar Mali da firaminista
2021-05-25 11:21:03 CRI
Rundunar hadin gwiwar bangarori daban daban ta MDD dake aikin wanzar da zaman lafiya a Mali (MINUSMA), a jiya Litinin ta wallafa wata sanarwa a shafinta na twita inda ta bukaci a sako shugaban rikon kwaryar kasar Mali, Bah N'Daw, da firaministan kasar Moctar Ouane.
MINUSMA ta kara da cewa, tilas ne a tabbatar da lafiyar shugabannin da ake tsare da su. Kuma tana ci gaba da tattaunawa da kungiyoyin ECOWAS da tarayyar Afrika AU, karkashin wani kwamitin sanya ido kan mika mulki na kasar, da sauran bangarori masu ruwa da tsaki na kasa da kasa dake taimakawa shirin mika mulkin kasar.(Ahmad)
Labarai Masu Nasaba
- An tusa keyar shugaban rikon kwaryar Mali da firaministan kasar zuwa sansanin sojan Kati da karfin tsiya
- Somaliya ba ta ji dadin matakin Kenya na haramta jiragen sama shiga kasarta ba
- Sojojin Somaliya sun kashe mayakan al-Shabab a kalla 7 a tsakiyar kasar
- Jami’in MDD yayi maraba da matakin maido yarjejeniyar zaben Somali