Gwamnatin Sudan ta nanata kudirinta na kare rayukan fararen hula a yankin Darfur da tashin hankali ya barke
2021-01-20 11:12:09 CRI
Gwamnatin Sudan ta sake nanata kudirinta na kare rayukan fararen hula da samar da tsaro a yankin Darfur, inda tashin hankalin kabilancin da ya barke a yankin ya yi sanadin rayukan gwamman mutane.
Wata sanarwar da ma’aikatar harkokin wajen kasar ta fitar, ta bayyana takaici kan yanayin tsaron da ake ciki a wasu sassan yankunan kudancin da yammacin Darfur. Ma’aikatar ta kuma sake nanata nauyin dake wuyan gwamnati, na tabbatar da tsaro da kare rayukan fararen hula a dukkan sassan kasar, inda yanzu haka, gwamnati da abokan hulda dake kokarin tabbatar da zaman lafiya, suke kara kaimi wajen sauke wannan nauyi.
Wasu alkaluma da ba na hukuma ba, sun nuna cewa, fadan kabilancin da ake ci gaba da gwabzawa a yankunan yammaci da kudancin Darfur, ya yi sanadin rayukan mutane 184, kana sama da mutane 200 kuma sun jikkata.(Ibrahim)
Labarai Masu Nasaba
- Yawan wadanda suka mutu sanadiyar harin ’yan bindiga a yammacin Darfur na Sudan ya kai 83
- Sudan na zargin Habasha da sabawa yarjejeniyar kan iyakokin kasashen
- Ga yadda sojojin kasar Sin wadanda suke tabbatar da zaman lafiya a Sudan suke murnar shiga sabuwar shekarar 2021
- Sudan ta nemi AU ta taka muhimmiyar rawa kan batun madatsar ruwan Habasha a tekun Nile