Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2008-10-21 18:31:30    
Shugabannin manyan addinai biyar na kasar Sin suna son ba da taimakonsu wajen tabbatar da zaman lafiya a Asiya da kuma duniya baki daya

cri

Yau ne aka rufe taron mabiya addinai daban daban na Asiya a karo na 7 domin samar da zaman lafiya, a birnin Manila, babban birnin kasar Philippines. An dai fara taron ne a ran 17 ga wata, kuma a lokacin taron, shugabannin manyan addinai guda biyar na kasar Sin suka bayyana wa wakilinmu cewa, suna son ba da nasu taimako wajen cimma burin tabbatar da zaman lafiya a nahiyar Asiya da kuma jituwa a duk duniya.

Taron na da taken "samar da zaman lafiya a Asiya", kuma wakilai fiye da 300 da suka zo daga kasashe da yankuna kimanin 30 sun hallara. Kwamitin zaman lafiya na addinai daban aban na kasar Sin shi ma ya tura wata tawagar da ke kunshe da wakilai 28 zuwa wajen taron.

Shugaban tawagar kuma mataimakin shugaban kwamitin kishin kasa na addinin katolika na kasar Sin, Mr.Liu Bonian yana ganin cewa, wadanda suka zo daga bangaren addinai na kasar Sin sun yi kokarin ba da ra'ayoyinsu dangane da samar da zaman lafiya a Asiya, wannan ya dace da manufar kwamitin zaman lafiya na addinan kasar Sin, ya ce,"A kasar Sin, addinai daban daban na zama daidai wa daida da juna, ba su taba samun rikici a tsakaninsu ba. Kwamitin zaman lafiya na addinan kasar Sin da ke kunshe da wakilan manyan addinai guda biyar na kasar Sin yana bin manufar sada zumunta da zaman lafiya da ci gaba da hadin gwiwa, kuma yana yada kyakkyawar al'adar kishin kasa da son zaman lafiya, kuma yana son bunkasa mu'amala da hadin gwiwa a tsakaninsa da kungiyoyin addinai na samar da zaman lafiya na duniya da yankuna da kuma na kasashe daban daban, don kiyaye dinkuwar kasa da kuma tabbatar da zaman lafiya da cigaba a duniya."


1 2