Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2008-07-09 09:40:20    
Kungiyar kwallon badminton ta kasar Sin tana yin namijin kokari domin shiga gasar wasannin Olympic ta Beijing

cri

A gun gasar cin kofin Thomas, kungiyar maza ta kasar Sin ta lashe kungiyar kasar Korea ta kudu da 3 bisa 1, sau uku ne ta rike da zakaran kofin Thomas. Wanda ya fi jawo hankulan 'yan kallo shi ne Lin Dan, a halin da ake ciki yanzu, Lin Dan ya zama matsayin koli a dandalin wasan kwallon badminton na duniya. Amma masu sha'awar wasan kwallon badminton na kasar Sin su kan damu da halinsa saboda wani lokaci a gun babbar gasa, hankalinsa ya kan tashi ba zato ba tsammani. Game da wannan, Lin Dan yana ganin cewa, shiga gasa mai wuya zai kyautata halinsa, ya ce:  "A wancen lokaci, na san gasar tana da wuya, amma ba zaben dake gabana, sai na kara yin kokari."

A gun wannan gasa, kungiyar kasar Sin ta samu zakarun kofin Thomas da kofin Uber lami lafiya, wannan ya sake shaida mana cewa, kungiyar wasan kwallon badminton ta kasar Sin tana matsayin koli a duniya. A sa'i daya kuma, 'yan wasan kasar Sin suna kara samun fasahohin gasa. Kafin gasar wasannin Olympic ta Beijing, kungiyar kwallon badminton ta kasar Sin za ta shiga gasanni a jere, haka kuma za ta kara kyautata halinta. (Jamila Zhou)


1 2