Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2008-03-25 11:02:04    
Wasu kafofin yada labaru na kasashen duniya sun yada hakikanan labaru kan lamarin da ya auku a birnin Lhasa

cri
 

Mr. Ken Wood ya alamanta cewa, a wuraren da 'yan Tibet suka wuce, sun jefa duwatsu kan kayayyakin da suka gani. "Sun kai farmaki kan wani tsoho, dan kabilar Han wanda ke kan keke. Sun jefe shi da duwatsu. Wasu tsofaffi 'yan kabilar Tibet sun fito sun yi kokarin hana su", a cewar Ken Wood.

Wannan mai yawon shakatawa da ya zo daga kasar Canada ya waiwayi wani labarin ceto daban. Ya ce, wani dan kabilar Han yana rokon 'yan Tibet wadanda suke yi masa barazana da duwatsu. "Sun harbe hakarkarinsa da kafafunsu, jini ya gudana kan fuskarsa duka. A wannan lokaci, wani Bature ya zo ya tayar da wannan dan kabilar Han. 'Yan Tibet wadanda suke da duwatsu a cikin hannayensu sun kewaye su biyu. Wannan Bature ya taimaki wannan dan kabilar Han, ya kada hannunsa ga sauran mutane. Daga karshe dai, 'yan Tibet sun yarda da ya kai wannan dan kabilar Han a wani wurin kare lafiyarsa."

Game da abubuwan da masu yawon shakatawa na kasashen yammacin duniya suka almanta, Thubten Samphel, wai kakakin gwamnatin Tibet wadda ke gudun hijira ya ce, wannan hargitsin nuna karfin tuwo hargitsi ne mai ban tausayi sosai. Ya kuma ce, "a kullum an nemi 'yan Tibet da su yi gwagwarmaya ba tare da nuna karfin tuwo ba."

A waje daya kuma, shafin yanar gizo na Australiya ya nuna cewa, a rana ta biyu bayan aukuwar hargitsin nuna karfin tuwo a Lhasa, wato ran 15 ga watan Maris, rundunar tabbatar da kwanciyar hankali ta kasar Sin ta rufe yankin Lhasa. Sun nemi masu yawon shakatawa da su zauna a cikin otel-otel da suke kwana. Amma a ran 17 ga wata, sun yarda da masu yawon shakatawa su fito su yi yawo a cikin birnin Lhasa. Amma dole ne su nuna fasfot nasu a tasoshin bincike.

Mr. Serge Lachapelle wanda ya zo daga Montreal na kasar Canada ya tuna da abubuwan da ya gani a wancan rana, cewar "an kone shaguna da yawa a birnin Lhasa. An kone kusan dukkan shagunan da ke gefunan tituna. An kuma lalata gine-gine da yawa."

Mr. Ken Wood ya kuma ce, "an rushe kusan dukkan yankunan musulmi. An kuma lalata dukkan shagunansu". "Jiya, wato ran 17 ga wata da safe, na iya fitowa daga otel na ci abinci a waje. Amma ban iya ganin murmushi a kan fuskar 'yan Tibet ba."  (Sanusi Chen)


1 2