Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2008-02-25 14:24:00    
Nazarin manufar Amurka kan Afirka bisa ziyarar da Bush ya kai wa Afirka

cri

Yana kasancewa da wani aiki da Bush bai gama ba tukuna a ziyararsa ta wannan karo. Har zuwa karshen ziyarar Bush a Afirka, ya zuwa yanzu dai ba a tabbatar da wurin da za a kafa hedkwatar sojojin Amurka a Afirka ba tukuna. Ko da yake Amurka ta sha aikawa da manyan jami'anta zuwa kasashen Afirka domin shawo kansu da su amince da shirin Amurka na kafa hedkwatar sojojin Amurka a Afirka, amma a halin yanzu sai Liberia kawai a bayyane ne ta bayyana fatanta na amincewa da hedkwatar sojojin Amurka a Afirka.

A lokacin ziyararsa, Bush ya sha yin karin bayani da cewa, kasarsa ba ta yi shirin kafa sabon sansanin soja a Afirka ba, nufin Amurka na kafa hedkwatarta ta sojoji a Afirka shi ne domin taimakawa kasashen Afirka wajen inganta karfinsu na kiyaye zaman lafiya da yaki da fasa-kwauri da kuma yaki da ta'addanci kawai. Amma ga alama Ghana da sauran kasashen Afirka suna nuna shakku sosai. A Liberia, kasa ce ta karshe da Bush ya kai ziyara, dukan bangarorin 2 ba su yi jawabi a bayyane kan batun zaben wurin kafa hedkwatar sojojin Amurka a Afirka ba. Bayan tashin Bush, shugaban Tanzania ya yi jawabin cewa, Tanzania ba ta da karfin kafa hedkwatar sojojin Amurka a Afirka ba. Don haka, cikin sauki ne muka iya gano cewa, ya zuwa yanzu dai kasashen Afirka ba su kwanta da hankulansu kan Amurka ba tukuna.

Bayan nazarin ziyarar Bush a wannan karo, wasu manazarta sun nuna cewa, nan gaba Amurka za ta kara ba da tasirinta a Afirka a harkokin siyasa da tattalin arziki, za ta ci gaba da karfafa habaka makamashi a Afirka, za ta kuma dauki matakai daban daban domin tabbatar da samun isasshen makamashi daga Afirka. A takaice dai, Afirka ta riga ta zama muhimmin bangare na manyan tsare-tsare da Amurka ke aiwatarwa a duk duniya.(Tasallah)


1 2