Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-03-04 18:12:23    
Ana mai da hankali kan batutuwan da ake fin yin tattaunawa a kan taruruka 2

cri

Bugu da kari kuma, a gun taruruka na shekarar bana, an fi mai da hankali kan maganganun da suke shafar aikin gona da manoma da harkokin kauyuka domin gwamnatin tsakiya ta kasar Sin ta bayar da manufofin raya sabbin kauyuka a nan kasar Sin. Mr. Fu Zhikang, wani wakilin majalisar dokokin kasar Sin wanda ya zo daga lardin Sichuan, ya ce, ko za a iya raya sabbin kauyuka da kyau, dole ne a ga ko manoma su samu moriya, ko za a iya daidaita maganganun da suka fi jawo hankulan manoma. Mr. Fu ya ce, "A gun wannan taro, zan nemi majalisar gudanarwa ta kasar Sin da ta kara zuba jari a cikin ayyukan noma, musamman a kan ayyukan yau da kullum da suke shafar tuddai da ruwa da gonaki da gandun daji da hanyoyi iri iri. Sabo da haka ne za a iya kafa tushe mai karfi domin karuwar hatsi da kudaden da manoma suke samu da kyautatuwar hanyoyin raya aikin gona."

Batutuwa daban da suke jawo hankulan jama'a su ne batutuwan da ke shafar zamantakewar jama'a. Kamar misali, kudaden karatu da makarantu suke karba suna da yawa yayin da kudaden likitanci da asibitoci suke karba suna da yawa da dai makamantansu. Yanzu gwamnatin kasar Sin tana kokarin daidaita irin wadannan maganganu.

Mr. Li Wen, wani kwadago mai ritaya ne da ke da zama a birnin Lanzhou na lardin Gansu yana da wani jika namiji wanda yake karatu a wata makarantar firamare ta kauye. Tun daga yanzu, jika namiji nasa ba zai biya kudin karatu ba domin gwamnatin tsakiya ta soke kudin karatu don daliban kauyuka wadanda suke karbar ilmin tilastawa a yankunan yammacin kasar Sin. Mr. Li Wen ya ce, wannan manufa tana da kyau. Yana fatan gwamnati za ta kara mai da hankali kan zamantakewar jama'a.(Sanusi Chen)


1  2  3