Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2005-11-23 18:30:26    
Kasar Sin ta kafa dokar rigakafin annobar murar tsuntsaye daga duk fannoni

cri

Yanzu muhimmin lokaci ne ga kasar Sin a wajen rigakafin annobar murar tsuntsaye. To, wadanne matakai ne kasar Sin ta dauka a wajen rigakafin annobar murar tsuntsaye. Kuma wane irin hukunci ne za a yanke wa mutane da sassan gwamnati domin ba su cika alhakin da ke bisa wuyansu ba? Duk wadannan tambayoyi an tanada su a cikin dokar gaggawa game da cututtukan dabbobi masu tsanani da majalisar gudanarwa ta kasar Sin ta bayar kwanakin baya. A cikin shirinmu na yau, sai ku saurari labarin da wakilin gidan rediyon kasar Sin ya ruwaito mana.

A gun taron bayar da labarum da ma'aikatar noma ta kasar Sin ta shirya jiya, Mr. Yin Chengjie, mataimakin minitan noma na kasar Sin ya bayyana cewa, a wajen rigakafin cututtukan dabbobi masu tsanani kasar Sin ta dauki matakai masu amfani. Dokar gaggawa game da cututtukan dabbobi masu tsanani ta kara kyautata dokokin kasar Sin a wajen rigakafin cututtukan dabbobi masu tsanani. Ya ce, Dokar gaggawa ta rigakafin cututtukan dabbobi masu tsanani ta zama jagora ga kasar Sin a wajen maganin cututtukan dabbobi.

Wannan doka ta tanada cewa, ofishin duba cututtukan dabbobi yana da nauyin duba cututtukan dabbobi bisa wuyansa, in ya samu rahoto kan cututtukan dabbobi masu tsanani ya kamata a aika da mutane zuwa wurin don duba halin da a ke ciki a wajen cututtukan dabbobi, kuma ya yi rahoto ga shugabansa cikin awa biyu. Cikin awa 4 da aka bullo da cututtukan dabbobi, ya kamata gwamnatocin larduna da sassan kula da cututtukan dabbobi su yi rahoto ga majalisar gudanarwa ta kasar Sin.

Wannan doka kuma ta tanada cewa, gwamnatin kasar Sin za ta ba da kyautar maganin rigakafin cututtukan dabbobi a wuraren da a ke yada cututtuka, ban da haka kuma gwamnatin kasar Sin za ta biya diyya ga mutanen da suka yi hasara sabo da an karkashe tsuntsayensu don rigakafin cututtukan tsuntsaye.

1  2