Masu bincike suna tsamani cewa, bayan kwamitin sulhu ya zartar da kuduri mai lamba 1636, game da bincike kisan gillar da aka yi wa Rifik Al-Hariri, Syria ta shiga halin wuya. Da farko, kwamitin binciken duniya yana bukatar kasar Syria ta ba da cikakken taimako, idan kasar Syria ba ta yi haka ba a lokacin da kwamitin ya yi bincike, kasar Syria za ta sami matsala sosai.
Na biyu, kwamitin binciken duniya ba shi da lokaci da yawa. Saboda kuduri mai lamba 1636 ya ba da ikon "daukin matakan cigaba" ga kwamitin sulhu, idan kasar Amurka da sauran kasashen Truai su ce kasar Syria ba ta ba da cikakken taimako, ta yadda za a dauki matakan cigaba ga kasar Syria kamar takunkumin karya tattalin arziki da harkokin waje, wannan zai sa kasar Syria ta fuskantar da motsi ya fi yawa daga kasashen duniya.
Masu bincike suna tsamani cewa, kasar Syria ta riga ta shirya sosai don ba da cikakken taimako ga kwamitin binciken duniya. Amma, shugaban kasar Syria Bashar Assad ya ki amsa tambayoyin kwamitin bunciken duniya, wannan wata matsalar da ke tsakanin kasar Syria da kwamitin, amma idan ana son a faro da halin gaskiyar kisan gilar, dole ne kasar Syria ta ba da cikakken taimako. [Musa] 1 2
|