Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Antonio Guterres ya yi Allah wadai da fille kan wasu kauyawa a Mozambique
2020-11-11 13:58:28        cri

Babban sakataren MDD Antonio Guterres, ya yi Allah wadai da kisan wasu kauyawa 50 wadanda 'yan bindiga suka yi a arewa maso gabashin kasar Mozambique.

A sanarwar da mai magana da yawun babban sakataren Stephane Dujarric ya fitar, mista Guterres, ya bayyana jimami game da faruwar lamarin a makon da ya gabata a lardin Cabo Delgado, inda ya bukaci hukumomin kasar da su kaddamar da bincike kan faruwar lamarin domin hukunta wadanda ke da hannu wajen aikata kisan.(Ahmad)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China