![]() |
|
2020-07-30 10:08:39 cri |
A cewar Jiang Wei, wani jami'in ma'aikatar jin dadjin al'umma ya fadawa taron manema labarai cewa, matakan da aka dauka sun hada da bayar da kudaden alawus-alawus, da bayar da kudaden rage radadi, da inganta hanyoyi da matakan neman tallafi.
Ya ce, wasu mutane da iyalai suna matukar bukatar agaji, sun hada da mutanen da suka rasa ayyukansu ko harkokin kasuwancinsu sakamakon annobar.
Jiang ya ce, gwamnatin tsakiya ta ware yuan biliyan 10.5 daga cikin sabon kasafin kudin da aka amince da shi wanda za'a taimakawa mutane masu fama da talauci wadanda annobar ta shafa. (Ahmad Fagam)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China