![]() |
|
2020-05-09 17:18:36 cri |
Firaministan kasar Masar Mostafa Madbouly ya sanar da cewa, za a ci gaba da aiwatar da matakan hana yaduwar cutar numfashi ta COVID-19 da ake bi yanzu har zuwa karshen watan Azumi. Ya kuma kara da cewa, ya kamata al'ummomin kasar su shiryawa yaki da cutar na dogon lokaci, sabo da cutar COVID-19 za ta ci gaba da kasancewa a duniya.
A nata bangaren, Jami'ar kula da harkokin taimakawa juna da raya zaman takewar al'umma da tabbatar da adalci da kula da iyalai ta kasar Morocco, Jamila EL Moussali ta ce, a halin yanzu, kasar Morocco na gudanar da babban aikin samar wa wadanda ba su da gidaje wuraren zama da ba a taba ganin irinsa ba cikin tahirin kasar.
Ita kuwa gwamnatin kasar Chadi sanarwa ta fidda, inda ta ce daga jiya 8 ga wata, za a hana shiga da fita a binrin N'Djamena, fadar mulkin kasar.
Haka kuma, shugaban kwamitin kula da yawon shakatawa da albarkatun kasa na majalisar dokokin kasar Tanzania ya bayyana cewa, ya dace a dauki matakan kawar da kudaden amfani da filayen jiragen sama ga kamfanonin jiragen sama, da rage farashin tikitin wuraren bude ido, da daukewa masu yawon shakatawa biza, da kuma rage harajin da masu zuba jari kan harkokin yawon shakatawa za su biya da dai sauransu, domin taimakawa farfadowar harkokin yawon shakatawa, ta yadda za a samu karin masu yawon shakatawa a kasar. (Maryam)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China