![]() |
|
2020-05-03 17:05:06 cri |
Kakakin ma'aikatar, Mr. Gao Feng ya bayyana cewa, har yanzu akwai wasu kamfanonin dake fuskantar matsalar karancin masu sayen kayayyakinsu da karancin kudin shiga. Ma'aikatar za ta hada kan sassan da abin ya shafa, don tsara manufofi na tallafawa kananan kamfanoni da ma kamfanoni masu zaman kansu, don sassauta kudin da suke biya wajen hayar ofisoshi. Ban da wannan kuma, ma'aikatar za ta aiwatar da gwajin samar da hidimar rayuwa a wasu unguwanni, don sa kaimi ga mazauna unguwanni wajen sayen kayayyaki. Sannan kuma, za ta aiwatar da shirin farfado da gidajen cin abinci, ta yadda za su bunkasa yadda ya kamata.(Lubabatu)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China