![]() |
|
2020-04-26 16:50:42 cri |
Kenyatta ya bukaci shugabannin kasashen duniya da cewa kada su kawar da kai wajen cigaba da yin hadin gwiwar yaki da sauran cutukan dake hallaka rayukan bil adama a sassan duniya.
Ya ce ranar Maleriya ta duniya tana kara baiwa alummar kasa da kasa damar yin nazari kan irin nasarorin da aka cimma a yaki da cutar, duk da cewa gwamnatoci na ci gaba da aiwatar da matakan kawo karshen cutar a nahiyar Afrika nan da shekarar 2030.
Ya ce, a kasar Kenya, gwamnatinsa ta yi matukar rage yaduwar cutar daga adadi mafi girma na masu kamuwa da cutar daga miliyan 6 zuwa miliyan 4.6 a cikin shekaru 10 da suka gabata. (Ahmad Fagam)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China