![]() |
|
2020-03-30 20:11:35 cri |
Yayin taron hukumar siyasa ta kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin da aka kira a ranar 27 ga wata domin tattauna yanayin tattalin arzikin da ake ciki a halin yanzu, kasar Sin ta tsai da kudurin farfado da masana'antu da kara habaka kasuwa a kasar, kana ta jaddada cewa, abu mai muhimmanci shi ne kara karfafa hadin gwiwar dake tsakanin kasa da kasa a bangarorin tattalin arziki da cinikayya, tare kuma kafa tsarin samar da kayayyaki tsakanin kasa da kasa, ta yadda za a tabbatar da jigilar kayayyaki a fadin duniya yadda ya kamata.
Yanzu annobar cutar numfashi ta COVID-19 tana yaduwa cikin sauri a fadin duniya, kasashe da dama sun rufe layukan zirga-zirgar jiragen sama, a don haka jigilar kayayyaki tsakanin kasa da kasa ta gamu da matsala, a irin wannan yanayi, kasar Sin tana ci gaba da kokari matuka domin tabbatar da jigilar kayayyakin ba da kariya domin ganin bayan annobar, ya zuwa ranar 26 ga wata, gaba daya hukumar zirga-zirgar jiragen saman kasar Sin ta tura jiragen sama 23 domin jigilar kayayyakin ba da kariya na yakar annobar, kayayyakin da kasar Sin ta yi jigilar su sun kai tan sama da 400.
A yayin taron kolin shugabannin kasashen mambobin G20 da aka kira ta kafar bidiyo, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayyana cewa, kasarsa za ta kara samar da magunguna da kayayyakin yau da kullum da kayayyakin ba da kariya ga kasuwar duniya, ta yadda za a taimakawa al'ummomin kasa da kasa da suke bukata.
Kamar yadda babban sakataren MDD Antonio Guterres ya rubuta a cikin wasikar da ya aika wa shugabannin G20, yanzu ya dace a hada kai a maimakon nuna kyama, kamata ya yi kasashen duniya su kara karfafa hadin gwiwar dake tsakaninsu domin kare lafiyar daukacin bil Adama.(Jamila)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China