2019-12-04 10:26:20 cri |
AU ta ce Afrika tana da damammakin bunkasa harkokin cinikinta a kasuwannin cikin gida. Don haka akwai bukatar kasashen Afrika su fadada harkokin kasuwanci a tsakaninsu domin ciyar da tattalin arzikinsu gaba da kuma cin moriyar kasashen.
A bisa kididdigar da kungiyar mai mambobi kasashen Afrika 55 ta fitar ya nuna cewa, hada hadar kasuwancin dake gudana tsakanin kasashen shi ne mafi kankanta da kashi 15 bisa 100, inda kasa da kashi 20 bisa 100 na kayayyakin da ake samarwa a nahiyar ne suke yawo a tsakanin kasashen.
Sakamakon bukatar da ake da shi a halin yanzu na cike gibin kasuwanci a tsakanin kasashen Afrika, AU ta kaddamar da muhimmin taro da nufin bunkasa mu'amalar cinikayya tsakanini nahiyar, daga ranar 3-5 ga watan Disamba a helkwatar kungiyar AU dake Addis Ababa na kasar Habasha, taken taron shi ne, "Kayayyaki kirar Afrika a yi cinikinsu a Afrika." (Ahmad Fagam)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China