Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2009-07-01 18:23:16    
Jam'iyyar kwaminis ta Sin na kara mai da hankali a kan sauraron ra'ayoyin jama'a domin inganta kanta a sabon halin da ake ciki

cri

Laraba 1 ga watan Yuli rana ce ta cika shekaru 88 da kafuwar jam'iyyar kwaminis ta Sin, wato jam'iyyar da ke jan ragamar mulkin kasar Sin. To, a cikin shekarun nan 88 da suka wuce, har kullum jam'iyyar na son sauraron ra'ayoyin jama'a domin inganta kanta. A gun taron ofishin siyasa na kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta Sin da aka kira a kwanan baya, an gabatar da daga matsayin gamsuwar jama'a a wajen binciken ayyukan shugabannin jam'iyyar. Sa'an nan kuma, babban sakataren kwamitin tsakiya na jam'iyyar, Mr.Hu Jintao ya jaddada cewa, a sabon halin da ake ciki, dole ne a dora muhimmanci a kan raya dimokuradiyya a cikin jam'iyyar, ta yadda za a gudanar da harkokin mulki bisa kimiyya da dimokuradiyya da kuma doka.
1 2 3