Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2009-11-09 14:46:09    
Algeriya ta yabawa kasar Sin bisa taimakawa kasashen Afirka cikin dogon lokaci

cri
A ran 8 ga wata, shugaban Algeriya Abdelaziz Bouteflika ya bayyana cewa, kasar Algeriya ta nuna babban yabo ga kasar Sin da ta nuna goyon baya ga kasashen Afirka domin samun adalci a cikin harkokin duniya, musamman ma a cikin shawarwari na Doha.

Bisa labarin da kamfanin dillancin labaru na gwamnatin Algeriya ya bayar, an ce, a gun bikin bude taron ministoci a karo na hudu na dandalin hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka da aka yi a birnin Sharm El Sheikh na kasar Masar, ministan tsaron kasar Algeriya, kana wakilin shugaban kasar Abdul-Aziz Belkhadem ya karanta bayanin malam Abdel Aziz Bouteflika, inda ya yi kira ga kasashen Afirka da Sin da su kara mu'amala a fannin tarbiyya da ma'aikata da kafofin yada labaru da hukumomin nazari, a yunkurin kara samun fahimta da girmama juna.(Fatima)