Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2009-11-09 08:57:00    
Wani jami'in kasar Zimbabwe ya yi fatan a inganta hadin gwiwa tsakanin kasarsa da kasar Sin zuwa wani sabon matsayi

cri
A kwanakin baya, gwamnan jihar Harare ta kasar Zimbabwe David Karimanzira ya bayyanawa 'yan jaridar kasar Sin cewa, kasarsa tana fatan sabbin matakan da aka gabatar a wajen taron ministoci na dandalin tattaunawa kan hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka a karo na 4 a birnin Alkahira za su inganta hadin gwiwa tsakanin Zimbabwe da Sin zuwa wani sabon matsayi.

A ran 6 ga wata, Karimanzira ya kai ziyara wajen bikin nunin hotuna kan nasarorin da aka samu bayan taron koli na Beijing na dandalin tattaunawa kan hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka a ofishin jakadancin Sin dake a kasar Zimbabwe. Ya kuma bayyana cewa, an sheda daga hotunan cewa, a karkashin dandalin tattaunawa kan hadin gwiwa tsakanin Zimbabwe da Sin an samu ci gaba a shekaru 3 da suka wuce. Ya yi imani cewa, sabbin matakan da aka gabatar a taron ministoci za su inganta hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu zuwa wani sabon matsayi, wanda zai inganta tattalin arzikin Zimbabwe.(Zainab)