Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2009-10-31 16:12:38    
Tawagar wakilan gwamnatin Sin ta fuskar al'adu ta kai wa Seychelles ziyara

cri
Ran 29 zuwa ran 30 ga wata, tawagar gwamnatin kasar Sin ta fuskar al'adu da ke karkashin shugabancin Cai Wu, ministan al'adu na kasar Sin ta kai wa kasar Seychelles ziyara a hukumance, bisa gayyatar da Vincent Meriton, ministan kula da bunkasa unguwanni da al'adu da wasannin motsa jiki da harkokin matasa na Seychelles ya yi.

A rakiyar Wang Weiguo, jakadan kasar Sin a Seychelles, tawagar Sin ta fuskar al'adu ta gai da James Michel, shugaban Seychelles, kuma ta yi shawarwari tare da Mr. Meriton, inda bangarorin 2 suka darajta dangantaka a tsakanin kasashen 2 a harkokin al'adu, kuma sun bayyana fatansu na ci gaba da inganta yin mu'amala da hadin gwiwa a tsakaninsu a harkokin al'adu.

Wannan ziyara wani bangare ne na harkar "mai da hankali kan kasar Sin ta fuskar al'adu a shekarar 2009" da kasar Sin ta shirya a kasashe fiye da 20 na Afirka daga watan Afrilu zuwa na Nuwamba a bana.(Tasallah)