Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2009-10-30 15:04:15    
Kasashen Chadi da Cameroon sun mai da hankali kan matsalar fari a shiyyar tabkin Chadi

cri
A ran 29 ga wata, shugaban Cameroon Paul Biya da takwaran aikinsa na Chadi Idriss Deby dake ziyara a kasar sun ba da wata hadaddiyar sanarwa cewa, kasashen biyu za su dauki matsayi daya a lokacin taron yanayi na Copenhagen, a kokarin yin kira ga kasa da kasa da su mai da hankali kan matsalar fari a shiyyar tabkin Chadi, da jaddada ba da kudin agaji ga tsarin halittu a wannan shiyya.

Bayan haka, sanarwar ta ce, kasashen biyu za su kara hada gwiwa, domin yaki da cinikayyar makamai ba bisa doka ba a yankin iyakacin kasa, da fashi a kan hanyoyi, da kuma saukaka takardar izni ta musanyar mutane da kayayyaki tsakaninsu.

A ran 29 ga wata, a filin jirgin sama, bayan da ya kammala ziyara a kasar Cameroon, Idriss Deby ya furta cewa, rikice-rikice a tsakiyar nahiyar Afirka suna ci gaba da kasancewa. Duk da haka, sabon yanayin da ake ciki a fannin siyasa zai taimakawa kasashe membobin kungiyar ECCAS a fannin samun bunkasuwa baki daya tare da sauran kasashen Afirka.(Fatima)