Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2009-10-28 14:42:09    
Shugaban kasar Senegal ya baiwa jakadan Sin dake a kasar lambar yabo

cri
A ran 27 ga wata a fadar shugaba, shugaban kasar Senegal Abdoulaye Wade ya baiwa jakadan Sin dake a kasar Lu Shaye lambar yabo ta kasar Senegal don nuna yabo gare shi da ya ba da gudummawa wajen raya dangantakar abokantaka ta hadin gwiwa tsakanin Sin da Senegal.

A yayin bikin bayar da lambar yabo, Mr Wade ya furta cewa, gwamnatin Senegal ta nuna babban yabo ga dangantakar hadin gwiwa tsakanin Sin da Senegal a fannoni daban daban, an sheda dukkan ayyukan da kasar Sin ta gudanar a kasar Senegal, gwamnatin Senegal da jama'arta sun nuna godiya game da wannan.

Karamin jakadan Sin na sashen kula da harkokin cinikayya na ofishin jadakan Sin dake a kasar Senegal Zhou Zhaoming ya bayyana cewa, tun bayan da aka sake kulla dangantakar diplomasiyya tsakanin Sin da Senegal a ran 25 ga watan Oktoba na shekarar 2005, bangarorin biyu sun gudanar da ayyukan hadin gwiwa da aka tabbatar a gun taron koli na Beijing na dandalin tattaunawa kan hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka, kana ana gudanar da yawancin manyan ayyukan ba da taimako ga kasar Senegal.(Zainab)