Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2009-10-27 15:43:56    
Kasar Nijeriya da kamfanin Sin sun daddale yarjejeniyar karin bayani kan gina hanyoyin jiragen kasa

cri

A ran 26 ga wata da yamma, ma'aikatar kula da harkokin zirga-zirga ta kasar Nijeriya da kamfanin ayyukan gine-gine na kasar Sin wato CCECC sun daddale yarjejeniya dangane da karin bayani kan gina hanyoyin jiragen kasa a tsakanin Abuja da Kaduna, wannan al'amari ya faru ne a Abuja, babban birnin kasar Nijeriya, abin da ya bayyana cewa, kasar Nijeirya ta sake fara gudanar da aikin gina hanyoyin jiragen kasa da aka tsayar a tsawon fiye da shekara daya.

Mataimakin babban manajan kamfanin CCECC Zhou Tianxiang da ministan kula da harkokin zirga-zirga na kasar Nijeriya su ne suka sa hannu kan yarjejeniyar da shafi karin bayani a madadin bangarorin Sin da Nijeriya. Zhou Tianxiang ya bayyana cewa, tsawon hanyoyin jiragen kasa a tsakanin Abuja da Kaduna ya kai kilomita 186.5, yawan kudin da aka tanada a yarjejeniyar ya kai dala miliyan 850, kana wa'adin yarjejeniyar ya kai tsawon watanni 36.(Zainab)