Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2009-03-05 11:08:12    
Kasashen Afrika suna bukatar tallafi don tinkarar matsalar kudi

cri
A ran 3 ga wata, shugaban Hukumar ba da lamuni ta duniya Dominique Strauss-Kahn ya yi gargadi cewa, matsalar kudi tana lalata sakamakon da yawancin kasashen dake kudancin Sahara suka samu a fannin tattalin arziki a shekaru goma da suka wuce. Kuma yawancinsu suna bukatar tallafi.

Bugu da kari, Mista Dominique Strauss-Kahn ya ce, yanzu kasa da kasa suna yin mu'amala mafi yawa, ba wadda za ta iya kaucewa matsalar. Ban da wannan kuma, kasashen Afrika da yawa ba su farfado daga mummunan tasiri na hauhawar farashin abinci da na mai ba, sabo da haka, kasashen suna fuskantar hali mafi tsamari.

Dadin dadawa, ya kiyasta cewa, kasashen Afrika za su bukaci karin jari daga hukumar ba da lamuni ta duniya. Kasashe 22 dake samun albashi kalilan ciki har da kasashen Afrika da yawa da suke shan fama da matsalar kudi. Ya kamata kasa da kasa za su ba da tallafin kudi na gaggawa a kalla dala biliyan 25 ga wadannan kasashe a bana don taimak musu.(Asabe)