Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2008-08-17 17:13:35    
Kasar Nijeriya ta shiga cikin gasar semi-final na wasan kwallon kafa bayan da ta lashe kasar Cote d'Ivoire biyu da ba ko daya

cri

Ran 16 ga wata da dare a filin wasa na Olympic na birnin Qinhuangdao, an yi gasar neman shiga cikin gasar semi-final ta wasan kwallon kafa maza ta wasannin Olympics na Beijing a tsakanin kungiyar kasar Nijeriya da kungiyar kasar Cote d'Ivoire, kasar Nijeriya ta lashe kasar Cote d'Ivoire biyu da ba ko daya, haka kuma ta shiga cikin gasar semi-final.

Yayin da ake yin wannan gasa, kide-kiden da abokanmu na kasar Afirka suke yi a wuri da ihun sa kaimi da 'yan kallo fiye da dubu 22 na kasar Sin suke yi sun yi musanya tare. A mintoci 44, 'dan wasa mai suna Odemwingie na kasar Nijeriya ya yi harbi mai dogon zango, kungiyar kasar Nijeriya ta ci gwal na farko.

A yayin da ke da sauran mintoci 9 kafin an gama gasa, kungiyar kasar Nijeriya ta sami damar buga Penalty. 'Dan wasa Obinna shugaban kungiyar wasan kwallon kafa ta kasar Nijeriya ya ci gwal na biyu.

A ran 19 ga wata da karfe 6 na yamma bisa agogon Beijing, wato karfe 11 na safe bisa agogon Nijeriya, za a yi gasar semi-final na wasan kwallon kafa a tsakanin kungiyar kasar Nijeriya da kungiyar kasar Belgium a birnin Shanghai da ke gabashin kasar Sin.