Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2008-08-12 14:17:34    
An sami babbar nasarar bikin bude gasar wasannin Olympic ta Beijing, a cewar shugaban Algeria

cri

Ran 11 ga wata kamfanin dillancin labaru na Algeria ya ba da labari cewa, shugaba Abdelaziz Bouteflika na kasar Algeria ya bayyana cewa, an sami babbar nasarar bikin bude gasar wasannin Olympic ta Beijing.

Labarin ya bayyana maganar Mr Abdelaziz Bouteflika cewa, gagarumin bikin bude gasar wasannin Olympic ta Beijing ya sami yabawa daga duk duniya. Kamar sakamakon da kasar Sin ta samu a sauran fannoni, nasarar bikin bude gasar wasannin Olympic ta Beijing ta bayyana cewa manufofin da shugabannin kasar Sin suka dauka suna dacewa sosai.

Mr Abdelaziz Bouteflika ya bayyana cewa, zuwa watan Disamba na shekarar bana, za a cika shekaru 50 na kulla huldar diplomasiyya tsakanin kasar Sin da kasar Algeria. Yanzu dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu tana bunkasuwa cikin hali mai kyau. Kuma suna da kyakkyawar makomar hadin gwiwa a fannin tattalin arziki da masana'antu. Yana sanya ran ga makomar dangantakar tsakanin kasashen Sin da Algeria.(Fatima)