A kwanakin nan, a gun shafin musamman na jaridar Nijeriya The Guardian, Olukayode Thomas, dan jaridar kasar Nijeriya wajen wasan motsa jiki ya bayyana abubuwan da ya gani lokacin da ya ba da labari wajen gasar wasannin Olympics ta Beijing. A cikin bayaninsa, bai manta da son baki na jama'ar Sin da kwararrun ayyukan da 'yan sanda na Sin suke yi ba.
Mr Thomas ya kawo wa kasar Sin ziyara ne a karo na farko, ya ce, ba a san ko kiran wasannin Olympics ne ya sanya musu yin haka ba, ko jama'ar Sin suna son baki tun asalinsu, suna taimakon baki da rashin nuna son kai. Idan ka bukaci gudummawa, za su fito su ba da taimako, ko da yake wannan ba aikinsu ba ne, amma za su taimake ka cikin farin ciki.
Tunanin Thomas kan 'yan sandan kasar Sin shi ne aiwatarwa da ladabi kuma tufaffinsu ya dace da halin da ke ciki. A ganinsa, 'yan sandan Sin sun yi aikinsu ta hanyar kimiyya da fasaha na zamani, sabo da haka suna da kwarewa. Ya ce, ba a samu laifuffuka a nan ba, kuma ba su kiyaye dokar zamantakewa ta hanyar nuna wa jama'a barazana ba.(Zainab)
|