Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2014-10-16 17:56:22    
Sin ta samar da gudummawar yaki da cutar Ebola da ta kai yuan miliyan 234

cri
Kakakin ma'aikatar harkokin kasuwanci ta kasar Sin Shen Danyang a ranar 16 ga wata ya bayyana a birnin Beijing cewa, tun bayan bullar cutar Ebola a wasu kasashen yammacin Afirka a farkon wannan shekara, kasar Sin a watan Afrilu da na Agusta da kuma Satumba ta samar da gudummawar da ta kai kudin Sin yuan miliyan 234 gaba daya ga kasashen da ke fama da cutar.

Shen Danyang ya bayyana hakan ne a gun taron manema labarai da ma'aikatar ta kasuwanci ta kasar Sin ta kira a wannan rana, inda a cewarsa, gudunmmawar ta shafi kayayyakin agaji da abinci da tsabar kudi da likitoci da kuma dakunan binciken cututtuka masu tafi da gidanka da sauransu.

Shen ya kara da cewa, a halin yanzu, kasar Sin ta kammala samar da gudummar da ta alkawarta a karo na farko da na biyu, a yayinda take kokarin tabbatar da gudummawar da za ta samar a karo na uku.

Shen ya ce, gwamnatin kasar Sin za ta samar da gudummawar da ta iya bisa ga yanayin da ake ciki da kuma bukatun kasashen da abin ya shafa, haka kuma za ta yi kokarin inganta hadin gwiwar kiwon lafiya a tsakanin Sin da Afirka, don taimakawa kasashen Afirka inganta kwarewar tinkarar cututtuka da tsarin kiwon lafiyar al'umma.(Lubabatu)