Ran 19 ga wata, He Yafei, wakilin kasar Sin da ke ofishin MDD a Gevena ya bayyana cewa, yanzu kasashen duniya suna dogaro da juna, kuma suna da moriya kusan iri daya a wasu fannoni, har ma ba a iya rabawa ba.
Ya bayyana hakan ne yau din nan alhamis yayin da yake gabatar da lacca data shafi horaswa kan manufofin tsaro.
Mr. He, makasudin ci gaban kasar Sin shi ne, kokarin neman samun bunkasuwa da jituwa a cikin tare da wadata jama'a, kana da kiyaye zaman lafiyar duniya .
Daga karshen Mr He ya kara jaddada cewa Kasar Sin tana fatan samun ci gaban kanta ta hanyar kiyaye zaman lafiya da ci gaban duniya, bayan haka kuma. ko da yaushe kasar Sin ta kan bi manufar samun zaman lafiya a duniya baki daya..(Maryam)
|