Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2009-11-10 09:42:23    
Kasar Sin za ta yi kokari wajen sa kaimi ga yin hadin gwiwa a fannonin aikin gona da manyan ayyukan yau da kullum a tsakaninta da kasashen Afirka

cri
A ran 9 ga wata, a gun taron ministoci a karo na hudu na dandalin tattaunawa kan hadin kai a tsakanin Sin da kasashen Afirka, ministan cinikayya na kasar Sin Chen Deming ya bayyana cewa, kasar Sin za ta ci gaba da bin manufar"dankon zumunci da zaman lafiya da hada kai da samun bunkasuwa", da yin kokari wajen karfafa yin hadin gwiwar tattalin arziki tare da kasashen Afirka, da kara ba da gudummawa ga samun bunkasuwar ayyukan gona da inganta kayan abinci da manyan ayyukan yau da kullum na kasashen Afirka.

A game da batun karfafa yin hadin gwiwa a fannonin aikin gona da manyan ayyukan yau da kullum a tsakanin Sin da kasashen Afirka, Chen Deming ya bayyana cewa, na farko, ya kamata a samu bunkasuwar aikin gona na kasashen Afirka, na biyu, ya kama a yi hadin gwiwa a fannin aikin gona a tsakanin Sin da kasashen Afirka ta sabuwa hanya, na uku, ya kamata a yi kokari wajen sa kaimi ga yin hadin gwiwa a fannin manyan ayyukan yau da kullum, na hudu, a kafa kyakkyawar gada ga kamfanonin Sin da na kasashen Afirka. Ya kamata bangarorin biyu su hada karfin wajen sa kaimi ga yin hadin gwiwa a fannonin aikin gona da manyan ayyukan yau da kullum a tsakaninsu.(Abubakar)