Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International Thursday    Apr 10th   2025   
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2009-10-15 18:05:03    
Za a kira taron ministoci na dandalin tattaunawar hadin kan Sin da Afirka a kasar Masar a wata mai zuwa

cri
Ma Zhaoxu, kakakin ma'aikatar harkokin waje ta kasar Sin ya bayyana a ran 15 ga wata a birnin Beijing, cewar za a kira taron ministoci a karo na hudu na dandalin tattaunawar hadin kan Sin da kasashen Afirka a kasar Masar a farkon watanni goma na wata mai zuwa. Kuma ya nuna cewa, taron zai taka muhimmiyar rawa da kara sa kaimi ga bunkasuwar dangantaka  a tsakanin Sin da kasashen Afirka, da kuma inganta hadin kan bangarorin biyu a fannoni daban daban.

Ma Zhaoxu ya kuma bayyana cewa, muhimmin aiki na taron shi ne kimanta yadda ake gudanar da matakan da aka yi alkwarin daukarsu a yayin taron koli na Beijing na dandalin tattaunawar, da kuma tsara shiri ga ayyukan hadin kan Sin da kasashen Afirka daga dukkan fannoni a shekaru uku masu zuwa. Kasar Sin tana son kara tuntubar dimbin kasashen Afirka, da kuma yin hadin kai tare da su domin aiwatar da kyawawan sakamakon da aka samu a yayin taron koli na Beijing, da kuma kira taron ministoci a karo na hudu na dandalin tattaunawar yadda ya kamata, ta yadda za a iya inganta hadin kan Sin da kasashen Afirka zuwa wani sabon mataki.(Kande Gao)

© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China. 100040