Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2009-10-15 18:05:03    
Za a kira taron ministoci na dandalin tattaunawar hadin kan Sin da Afirka a kasar Masar a wata mai zuwa

cri
Ma Zhaoxu, kakakin ma'aikatar harkokin waje ta kasar Sin ya bayyana a ran 15 ga wata a birnin Beijing, cewar za a kira taron ministoci a karo na hudu na dandalin tattaunawar hadin kan Sin da kasashen Afirka a kasar Masar a farkon watanni goma na wata mai zuwa. Kuma ya nuna cewa, taron zai taka muhimmiyar rawa da kara sa kaimi ga bunkasuwar dangantaka  a tsakanin Sin da kasashen Afirka, da kuma inganta hadin kan bangarorin biyu a fannoni daban daban.

Ma Zhaoxu ya kuma bayyana cewa, muhimmin aiki na taron shi ne kimanta yadda ake gudanar da matakan da aka yi alkwarin daukarsu a yayin taron koli na Beijing na dandalin tattaunawar, da kuma tsara shiri ga ayyukan hadin kan Sin da kasashen Afirka daga dukkan fannoni a shekaru uku masu zuwa. Kasar Sin tana son kara tuntubar dimbin kasashen Afirka, da kuma yin hadin kai tare da su domin aiwatar da kyawawan sakamakon da aka samu a yayin taron koli na Beijing, da kuma kira taron ministoci a karo na hudu na dandalin tattaunawar yadda ya kamata, ta yadda za a iya inganta hadin kan Sin da kasashen Afirka zuwa wani sabon mataki.(Kande Gao)