Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2009-10-15 14:55:02    
Musulman kasar Sin dubu 12.7 za su je kasar Saudiyya a bana don yin aikin Hajji

cri
Musulman kasar Sin dubu 12.7 za su je kasar Saudiyya a bana don yin aikin Hajji, adadin ya fi na bara da dari 7, tawagar maniyyata ta farko za ta tashi a karshen watan da muke ciki.

Mataimakin shugaban kungiyar addinin musulunci ta kasar Sin kuma shugaban tawagar maniyyata Yang Zhibo ya bayyanawa 'yan jarida a ran 15 ga wata cewa, musulman da za su yi aikin Hajji a bana sun zo ne daga larduna da birane 27 a kasar Sin, kuma yawan maniyyata daga jihar Xinjiang ya wuce dubu 3, wanda ya zama matsayin koli a kasar.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, tawagar za ta tashi daga kasar Sin cikin rukuni-rukuni tun daga ranar 30 ga watan Oktoba zuwa ranar 17 ga watan Nuwamba, bayan da suka kammala yin aikin Hajji, za su komo kasar Sin cikin rukuni-rukuni tun daga ranar 3 zuwa 21 ga watan Disamba.(Zainab)