Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2009-03-23 19:52:10    
Akwai kasashe da kungiyoyin kasa da kasa 233 wadanda suka tabbatar da halartar bukin baje-koli na kasa da kasa da za'a yi a birnin Shanghai

cri
Wata majiya daga shafin Internet na bukin baje-koli na kasa da kasa ta ce, kasar Belize wadda ke arewa maso gabashin tsakiyar nahiyar Amurka, ta tabbatar da cewa, za ta halarci bukin baje-koli na kasa da kasa da za'a shirya a birnin Shanghai na kasar Sin a shekara ta 2010. Zuwa ranar 23 ga wata, akwai kasashe da kungiyoyin kasa da kasa da adadinsu ya kai 233 wadanda suka bada tabbacin halartar bukin baje-koli na kasa da kasa da za'a yi a birnin Shanghai.

Kasar Belize, da sauran kasashen yankin Caribbean guda 10, gami da kungiyar hadin-kan kasashen Caribbean za su shirya nune-nune cikin hadin-gwiwa a dakin nune-nune na kungiyar hadin-kan kasashen Caribbean.

Har yanzu kasar Sin ba ta kulla dangantakar diflomasiyya a tsakaninta da kasar Belize. A halin da ake ciki yanzu, yawan kasashen da ba su kulla huldar diflomasiyya tare da kasar Sin ba wadanda suka tabbatar da halartar bukin baje-kolin ya kai 17.(Murtala)