Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2009-03-02 20:07:00    
Membobin majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta Sin sun mai da hankali kan shawara dangane da tattalin arziki

cri
A ran 2 ga wata, Mr Zhao Qizheng, kakakin taro a karo na biyu na majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta kasar Sin na 11 ya bayyana cewa, ya zuwa ran 2 ga wata da karfe 12 na tsakiyar rana, ofishin sakatariya ya samu shawara 265 da suke shafar tattalin arziki, kamar kara bukatun jama'a a cikin gida da inganta cinikayya a yankin iyakar kasar Sin da sauransu, sun fi jawo hankali.

A gun taron manema labaru dangane da taron da aka shirya a karo na farko a ran 2 ga wata, Mr Zhao ya gabatar da cewa, kwamitin tsakiya ya bayar da shirin kebe yuan biliyan dubu 4 a cikin shekaru 2 masu zuwa domin karawa tattalin arziki kaimi, kuma membobi da yawa sun bayyana ra'ayin cewa, abu mafi muhimmanci shi ne yin amfani da kudin yuan biliyan dubu 4 yadda ya kamata, kada a dinga maimaita wasu ayyuka sau da yawa, dole ne a yi amfani da kudin wajen kyautata zaman rayuwar jama'a.

Kuma Mr Zhao ya bayyana cewa, membobin majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa sun mai da hankali sosai kan raguwar cinikayya a iyakar kasar Sin, da yadda za a kara cinikayya a wannan yanki. Dadin dadawa, sun mai da hankali kan batun kara samar da guraban aikin yi da rage gibin dake tsakanin birane da kauyuka da sauransu.

Za a kaddamar da taro a karo na biyu na majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa na 11 a ranar 3 ga wata da karfe 3 na yamma a babban dakin taron jama'a, kuma za a rufe taron ne a ranar 12 ga wata da safe, wanda zai dauki tsawon kwanaki 9 gaba daya.(Fatima)