Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2008-12-20 20:12:18    
Sin ta dauki matakai da dama don tabbatar da zaman rayuwar jama'a a yankunan da girgizar kasa ta shafa cikin hunturu

cri
Domin tabbatar da zaman rayuwar jama'a cikin lokacin hunturu yadda ya kamata a yankunan da girgizar kasa ta galabaitar da su, ma'aikatar kula da harkokin jama'a ta kasar Sin ta yi kokarin fahimtar bukatunsu tare kuma da daukar dimbin matakai.

Matakan da ma'aikatar ta dauka sun hada da kira al'umma su ba da taimakon kayan sutura, don daidaita matsalar karancin sutura da ake fama da ita a yankunan da bala'in ya shafa. Sa'an nan, ta sa kaimi ga farfado da gidajen manoma da suka lalace sakamakon bala'in, kuma manoma wadanda ba su da gidajen kwana za su iya samun kudin taimako da yawansu ya kai yuan dubu 20. Ban da wannan, a ran 13 ga wata, ma'aikatar kula da harkokin jama'a tare kuma da ma'aikatar kudi ta kasar Sin sun ware kudaden da yawansu ya kai kudin Sin yuan biliyan 1 da miliyan 800 don taimaka wa jama'ar da ke yankunan da bala'in ya shafa.(Lubabatu)