Ran 19 ga wata, a nan Beijing, ma'aikatar harkokin waje ta kasar Sin da kuma kwamitin shirya gasar wasannin Olympic ta Beijing sun shirya liyafa domin nuna wa kasashen duniya godiya saboda sun mara wa kasar Sin baya wajen yin gasar wasannin Olympic ta Beijing da ta nakasassu. Mataimakin shugaban kasar Sin Xi Jinping ya halarci liyafar, ya kuma ba da jawabi.
A madadin gwamnatin Sin da jama'ar Sin, a cikin sahihanci ne Mr. Xi ya nuna godiya ga wadanda suka ba da gudummowa wajen samun cikakkiyar nasarar gudanar da gasar wasannin Olympic ta Beijing da ta nakasassu. Ya bayyana cewa, an rufe gasar wasannin Olympic ta Beijing da ta nakasassu ta shekara ta 2008 daya bayan daya. Kasasr Sin ta cika alkawarin da ta yi a tsanake, wato shirya gasar wasannin Olympic mai halin musamman kuma bisa babban mataki, da kuma shirya gasar wasannin Olympic ta nakasassu kamar yadda aka shirya gasar wasannin Olympic.(Tasallah)
|