Yau ranar 22 ga wata ne aka shiga kwana na 14 da soma gasar wasannin Olympics, za a fitar da lambobin zinariya 21 a wannan rana. Ya zuwa karfe 9 na dare bisa agogon Beijing, an riga an fitar da lambobin zinariya 15. Kasar Nijeriya ta samu lambobin tagulla biyu.
A cikin gasar tseren kwale-kwale ta mita 1000 tsakanin maza biyu biyu, kungiyar 'yan wasan kasar Jamus ta samu lambar zinariya.
A cikin gasar tseren kwale-kwale ta mita 1000 tsakanin maza hudu hudu, kungiyar 'yan wasan kasar Belorussia ta samu lambar zinariya.
A cikin gasar gudu ta mita dubu 5 ta mata, 'yar wasa ta kasar Habasha Tirunesh Dibaba ta samu lambar zinariya.
Ban da haka kuma, a cikin gasar dogon tsalle ta mata, 'yar wasa ta kasar Nijeriya Okagbare Blessing ta samu lambar tagulla. 'Yar wasa ta kasar Brazil Maggi Higa ta samu lambar zinariya.
Kuma a cikin gasar gudu ta ba da sanda tsakanin mata hudu na mita 4, kungiyar 'yan wasan kasar Nijeriya ta samu lambar tagulla. Kungiyar kasar Rasha ta samu lambar zinariya.
|