Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2008-08-01 22:22:08    
Jakadan kasar Sin a Mauritius ya yi ban kwana da shugaban kasar da zai tashi zuwa birnin Beijing don halartar bikin bude wasannin Olympics

cri
Jiya 31 ga watan Yuli, jakadan kasar Sin a Mauritius, Mr.Gao Yuchen ya kira liyafa, don yin ban kwana da shugaban kasar Mauritius Anerood Jugnauth, da kuma matarsa, wadanda za su tashi zuwa birnin Beijing don halartar bikin bude wasannin Olympics.

Mr.Jugnauth ya nuna babban yabo a kan huldar aminci da hadin gwiwa da ke ta bunkasa a tsakanin kasarsa da Sin. Ya ce, duk duniya na zura ido a kan wasannin Olympics na Beijng. Ya nuna yabo a kan babban kokarin da gwamnatin kasar Sin da jama'arta suka yi wajen share fagen wasannin Olympics, kuma yana da imanin cewa, wasannin Olympics na Beijing zai kasance wasannin da ya fi samun nasara kuma kasaita a tarihi.(Lubabatu)