Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2008-07-29 19:33:38    
Kasar Sin za ta kare ikon mallakar ilmi na Olympics a tsanake

cri

Darektan kula da ka'idoji na hukumar kare ikon mallakar ilmi ta kasar Sin, kuma kakakin hukumar Mr. Yin Xintian ya bayyana a gun wani taron manema labaru da aka shirya a cibiyar watsa labarai ta duniya da ke birnin Beijing a ran 29 ga wata cewa, kasar Sin za ta kare ikon mallakar ilmi na Olympics a tsanake.

Mr. Yin ya ce, gwamnatin kasar Sin ta kaddamar da ka'idojin kare alamun Olympics da kuma aiwatar da su, domin kare alamun Olympics, da tabbatar da halaliyar moriya ta mutanen da suke da ikon mallakar ilmi wajen samar da alamun Olympics, da kiyaye mutumcin gasar wasannin Olympics. Wadannan ka'idoji sun zama hakikanan matakai da kasar Sin ta dauka wajen kare ikon mallakar ilmi na Olympics.(Danladi)