Wasannin Olympics na lokacin hunturu da za a gudanar da su a idon Xi Jinping
2021-07-20 16:25:35 CMG
Sauran wasu kwanaki 199 a fara gudanar da wasannin Olympics na lokacin hunturu karo na 24 a birnin Beijing na kasar Sin. Inda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya dora muhimmanci sosai kan wannan biki, saboda yana fatan yin amfani da wannan dama wajen janyo hankalin karin mutanen kasar Sin fiye da miliyan 300 domin su shiga wasanni masu alaka da kankara.
Ban da wannan, shugaban na kasar Sin ya bukaci a yi amfani da fasahohin zamani, don karbar bakuncin wasannin Olympics da kyau, ta yadda kasar za ta samu cika alkawarin da ta yi wa mutanen duniya, na gudanar da wani kasaitaccen biki mai matukar burgewa. (Bello Wang)