Ministan harkokin wajen kasar Sin zai halarci taron dandalin zaman lafiya na duniya karo na 9
2021-07-02 20:40:37 CRI
Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Wang Wenbin, ya bayyan Jumma’ar nan cewa, mamban majalisar gudanarwar kasar Sin kana ministan harkokin wajen kasar Wang Yi, zai halarci bikin bude taron dandalin zaman lafiya na duniya karo na 9 tare da gabatar da jawabi.
Taron da zai gudana daga gobe Asabar 3 zuwa 4 ga watan Yuli, zai a yi shi ne a jami’ar Tsinghua dake nan birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin.(Ibrahim)
Labarai Masu Nasaba
- Ministan harkokin wajen kasar Sin zai halarci taron ministocin harkokin wajen kasashe mambobin G20
- Wang Yi ya halarci liyafar ranar Afirka da aka shirya a Beijing
- Wang Yi zai jagoranci taron kwamitin sulhun MDD kan rikicin Isra’ila da Palestine
- Ministan harkokin wajen Sin ya bayyana matsayar Sin kan rikicin Falastinawa da Isra’ila